Za a farfado da Cibiyar Koyon Harshen Faransanci a Katsina

520

Daga Isah Miqdaf

Gwamnatin Jihar Katsina karkashin jagorancin Malam Dikko Umaru Radda, PhD, CON, tare da hadin gwiwar shirin AGILE sun gyara makarantar Katsina Billingual School da ke SUNCAIS, a cikin Birnin Katsina.

Haka zalika, Gwamna Radda ya amince da sake farfado da Cibiyar koyan harshen Faransanci da za su ci gaba da gudanar da karatu a makarantar wanda za’a rika gudanar da shirin shaidar difloma da wasu kwasa-kwasai a cikin harshen Faransanci.

Cibiyar Koyon Harshen Faransanci da ke jihar Katsina a Najeriya, tana da fa’idodi da yawa na ilimi da suka hada da samun damar guraben karatu ga É—aliban Katsina don yin karatu a Faransa, ba da darussa, bita, da takardun shaida cikin harshen Faransanci, adabi, da al’adu da kuma haÉ“aka sha’awar aiki a Æ™ungiyoyin Æ™asa da Æ™asa, diflomasiyya da sauran su.

Haka zalika, wannan cibiyar za ta bada damar koyon harshen Faransanci da al’ada, haÉ“aka Æ™warewar sadarwa don dangantakar Æ™asa da Æ™asa, tafiye-tafiye, da kasuwanci.

Wannan kuduri ba karamin ci gaba zai kawo ba a harkar ilimi a Jihar Katsina ta dalilin kyakyawan Shugabanci na Mai Girma Gwamna Malam Dikko Umaru Radda

Warning: A non-numeric value encountered in /home/kunnenga/public_html/wp-content/themes/Newspaper/includes/wp_booster/td_block.php on line 1009

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here